📻 Labaran Hausa

DA ƊUMI-ƊUMI: Shin Ko Kun San Cewa Mawaƙi Hamisu Breaker Ya Yi Aure Watanni Bakwai Da Su Ka Wuce ?

DA ƊUMI-ƊUMI: Shin Ko Kun San Cewa Mawaƙi Hamisu Breaker Ya Yi Aure Watanni Bakwai Da Su Ka Wuce ?

DA ƊUMI-ƊUMI: Shin Ko Kun San Cewa Mawaƙi Hamisu Breaker Ya Yi Aure Watanni Bakwai Da Su Ka Wuce ?

DAGÀ Shafin Dokin Karfe TV

Labarin da ke shigowa Ofishinmu na Jaridar Dokin Ƙarfe TV da ɗumi-ɗumi yanzu-yanzu, wata majiya mai tushe ta tabbatar mana da cewa fitaccen mawaƙin Hausa, Hamisu Breaker Ɗorayi ya yi aure cikin sirri tsawon watanni bakwai da su ka wuce.

Hamisu Breaker, babban mawaƙi ne mai rere waƙoƙin soyayya masu ratsa zuciya cikin harshen Hausa, wanda ko da a ƴan kwanakin da su ka gabata an yi ta cece-ku-ce akansa biyo bayan wasu kalamai da abokiyar sana’arsa wacce ta ke taka rawa cikin waƙensa, Rakiya Musa ta yi cikin hira da Hadiza Gabon inda wasu ke zargin cewa da Hamisu Breaker ɗin ta ke irin yadda ta siffanta tsananin soyayyar da ta ke yi wa wani mutum tun kafin ya samu ɗaukaka.

A binciken da Jaridar Dokin Ƙarfe TV ta gudanar ta gano cewa tabbas Hamisu Breaker ya yi aure a wani yanayi mai kama da sirri tayadda hatta abokan sana’arsa a masana’antar Kannywood ba kowa ne ya sani da auren ba sai ƴan ƙalilan.

Shin ko mai ya sa babban jarumin mawaƙi kamar Breaker ya yi aure cikin sarri duk da irin ɗaukaka da shuhurar da ya ke da ita ?, Shin masu karatu mai za ku ce ?

Ban Sa A Kama Hamisu Breaker Ba, Cewar Adam Fasaha

Fitaccen mawakin nan, Adam Fasaha ya musanta jita-jitar da ake ta yadawa cewa ya kama abokin sana’arsa mawaki Hamisu Breaker bisa zargin sa sa yaudaro tsohuwar matarsa, Momi Gombe zuwa cikin masana’antar fim.

Idan ba a manta ba, tun bayan da Adam Fasaha ya zargi Hamisu Breaker din ne aka soma yada wasu hotuna da aka nuna jami’an tsaro sun kama mawaki Breaker, wanda kuma hotunan an yi su ne da sunan wasa a yayin wani wasa da Breaker ya gudanar a cibiyar wasanni ta Abacha Youth Center dake Kano a shekarun baya.

A yayin da yake jawabi ta bakin Adam Fasaha, mawaki Aliliyo Mai Waka ya bayyana cewa wasu daga cikin yaran Hamisu Breaker din ne suke ta yada hotunan domin su jawowa Adam Fasaha zagi.

“Ni Aliliyo Mai waka ina da tabbacin wannan hoton da suke yawo da shi suna cewa wai mun kama Hamisu Breaker ba mu da masaniya akan hakan, suna yin haka ne domin su ga sun wanke kansu daga wancan zargin da ake yi Breaker din. Ko da ba mu kama Hamisu ba kamun da Allah kawai zai yi masa shine babban kamu amma Adam Fasaha ba shi da hannu kan hakan.

“Sannan Hamisu ya bani mamaki da wai yake cewa wai mun yi masa kage. Ya manta ka taba tura min sako (message) ka ce mun ko yanzu Adam Fasaha idan yana son Momy kai kadai za ka sa ta koma gidansa. Ka manta ka ce mun kai ka bawa Momy Gombe damar auran Adam Fasaha kuma ka ce mun ni ban isa na yi komai a kai ba.

“Haka kuma ka ce yadda Momy take jin maganarka ko ta mahaifanta ba ta ji kuma kace kai ne ka bata kwarin gwiwar aure.

“Amma zan yi maka tambaya, mai ya sa lokacin da Momy ta fito daga gidan Adam Fasaha har kawo yanzu baka taba kiran sa ba ka ce mai ya faru tsakaninsa da Momy. A matsayin ka na wanda ya san ta yi aure mai ya sa ka dauke ta a satin kuka tafi shutin din fim. Ina tambayar ka wannan ma kage ne?

Sannan akwai wata jaruma daga cikin kawayen Momy Gombe amma ta ce a sakaye sunanta ta ce tabbas Hamisu Breaka da Momy sun ci amanar Adam Fasaha kuma Allah kadai zai yi saka masa.

Daga karshe Adam Fasaha ya godewa Ali Nuhu kan yadda ya yi ruwa da tsaki kan rikicin don ganin ya daidaita lamarin. Ba kamar sauran abokan sana’ar su ba da suka dinga rura wutar rikicin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button