.
📻 Labaran Hausa

DA ƊUMI-ƊUMI: Gawuna ya taya Abba K. Yusuf murna

DA ƊUMI-ƊUMI: Gawuna ya taya Abba K. Yusuf murna

DA ƊUMI-ƊUMI: Gawuna ya taya Abba K. Yusuf murna

Ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamna a jihar Kano, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, ya taya Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP, wanda ya lashe zaɓen da ya gudana a ranar 18 ga watan Maris.

A wani sako na murya ta manhajar WhatsApp, wanda kakakin sa, Hassan Musa Fagge ya saki a yau Laraba, Gawuna ya yi wa Abba Gida-Gida addu’ar cewa Allah Ya sa ya zama shugaba na gari.

Daily Nigerian Hausa na ruwaito a cewar Gawuna, tun bayan da hukumar zaɓe, INEC ta sanar da Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaɓen, jam’iyyar APC ta rubuta ƙorafe-ƙorafe kan cewa a yi duba a sakamakon zaɓen domin akwai kura-kurai.

Ya kara da cewa duk da wannan yunkuri da APC ta yi na a sake tantance sakamakon zaɓen tare da sake zabuka a wasu gurare, sai INEC ɗin ta baiwa Abba shaidar lashe zabe a yau Laraba.

“Sabo da haka, tunda hukumar zaɓe ta daɗa tabbatarwa da Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP zaɓen a yau 29 ga watan Maris, to ina mai tunawa magoya bayan mu cewa tun a baya min yi addu’a cewa in alheri ne, Allah Ya bamu, in kuma babu alkhairi, Allah Ya canja mana da abinda ya fi alkhairi.

“Shi kuma wanda ya ci zaɓen, muna masa addu’ar Allah Ya sa ya zama shugaba na gari.

“Mu na yi wa magoya bayan mu godiya bisa fitowa da suka yi kazan su da matan su suka zaɓe mu. Mu na godiya kuma ina kira ga magoya baya da mu zamana masu yadda da ƙaddara.

“Mu ma addu’a Allah Ya sa mu zama masu biyayya ga shugabanci da kuma bin doka. Allah Ya bamu lafiya da zama lafiya,” in ji Gawuna.

Awani labarin kuma

Babban dalilin da yasa nake kira a zabi Ganduje – Inji Sheikh Kabiru Gombe

Babban Malamin addinin Musulunci, kuma sakataren kungiyar Jama’atil Izalatil Bidi’a wa Iqamatissunnah, Sheikh Kabiru Gombe ya bayyana wani kwakkwaran dalilin da ya kamata jama’ar jahar Kano su sake zaban Gwamna Abdullahi Ganduje a karo na biyu.

Majiyarmu ta ruwaito Kabiru ya bayyana haka ne cikin wani jawabi da yayi kuma aka nada, da a yanzu haka yake yawo a kafafen sadarwar zamani ana watsa shi, inda yace babban dalilin da zai fada ma Allah idan Ya tambayeshi akan me yace a zabi Ganduje shine Musuluntar da Maguzawa.

A jawabin nasa, Shehin Malamin ya bayyana yadda Gwamna Ganduje ya taba gayyatarsu zuwa Musuluntar da wasu maguzawa su dari biyu, da kiristoci guda biyu da suka nuna sha’awar shiga Musulunci.

“Allah Ya sani kuka na dinga yi a ranar da muka tafi musuluntar da maguzawan, saboda naga abinda ban taba gani ba, na san irin wahalar da muke sha idan muka shiga garin arna ko maguzawa kafin mu samu mutum 10 sun karbi musulunci, tare da bata tsawon lokaci. Amma sai gashi abin mamaki mutane 202 zasu musulunta a gabana, zasu karbi Kalmar shahada.” Inji shi.

Malam Kabiru ya kara da cewa shi da kasan mutane 20 ya baiwa shahada, shima shugaban kungiyar Izala, Sheikh Abdullahi Bala Lau mutane 30 ya baiwa shahada, sai gwamnan jahar Kano daya baiwa kusan mutane 50 shahada, haka nan Shekarau ma ya bada shahada ga mutane 30.

Malamin yace haka sauran Maluma suka biyo baya suka yi ta baiwa maguzawanann Kalmar shahada, anayi ana canza musu suna, inda suke zaban sunan daya kwanta musu na Musulunci, har yace a gabansa wani mutumi ya bayyana musu cewa sunansa na yanka Jemage.

Daga karshe shehin Malamin ya tabbatar da cewa bayan kammala musuluntar da maguzawan, sai Ganduje ya raba musu kyautar kayan alheri, inda mata suka samu turmin zani da atamfa da jarin kudi, Maza kuma suka samu turmin shadda da jari.

Munsamo wannan rahotan daga shafin hausa loaded .

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button