.
📻 Labaran Hausa

An kama wani magidanci bayan ya cinnawa matar sa da ‘yayan sa wuta sabida taki amincewa suyi kwanciyar aure

An kama wani magidanci bayan ya cinnawa matar sa da ‘yayan sa wuta sabida taki amincewa suyi kwanciyar aure

An kama wani magidanci bayan ya cinnawa matar sa da ‘yayan sa wuta sabida taki amincewa suyi kwanciyar aure

Wani magidanci ya cinnawa ‘yayan matar sa guda biyar wuta bayan ta hana shi suyi kwanciyar aure.

Magidancin mai suna “Ojo Joseph” mai shekara 54 a duniya ya aikata wannan aika-aikar ne a jihar Ondo, lamarin ya auku ne a unguwar Fagun cikin garin Ondo a ranar Lahadi 6 ga watan Oktoban 2022 dasafe, kamar yadda “Labarun Hausa” suka ruwaito.

Joseph ya fusata ne inda ya cinnawa yaran wuta bayan mahaifiyar su taki yarda suyi kwanciyar aure.

Daya daga cikin yaran ya kone har lahira yayin da sauran suka samu munanan raunika inda ake duba lafiyar su a babban asibitin tarayya dake Owo.

Matar sa da tagwayen da suka haifa tare masu watanni sha takwas aduniya sun tsira daga wutar da ‘yan kananan raunika.

Da take tabbatar da aukuwar lamarin, kakakin hukumar ‘yan sandan jihar “Funmi Odunlami” ta bayyana cewa, tuni aka kama magidancin.

Ta kuma kara da cewa, an fara gudanar da bincike sannan za’a kammala kafin a tura wanda ake zargin zuwa kotu bisa zargin sa wuta da kisan kai.

Rahoto daga Labarun Hausa

Kotu ta sanya ranar da za’a saurari karar da ake yiwa dan china daya kashe Ummita

Wata babbar kotun jihar Kano wacce mai shar’a Sanusi Ado Ma’aji ke jagoranta, ta daga sauraron karar da ake yiwa dan kasar Chana “GengQuangrong” wanda ake tuhuma da kisan masoyiyar sa, Ummul kulsum Sani Buhari wacce aka fi sani da Ummita.

Alkalin ya daga sauraron karar ne bisa rashin halartar lauyan dake kare wanda ake tuhumar, kamar yadda “Labarun Hausa” suka ruwaito.

A yayin da aka cigaba da sauraron karar a ranar Alhamis “Geng Quangrong” ya roki kotun data daga sauraron karar domin ya samu damar tuntubar lauyan sa domin wakiltar sa.

Da yake mayar da martani Antoni janar na jihar Kano “Musa AbdullahiLawan” bai nuna kin amincewa da bukatar wanda ake kara ba ta a daga sauraron shari’ar.

Lauyan gwamnatin yace: Tabbas ba zamu iya cigaba da wannan shari’ar
ba babu lauya, mai kare wanda ake kara wannan shine tsarin.

A bisa halin da ake ciki mun nemi a daga sauraron karar na dangajeran lokaci domin bada dama ga wanda ake kara ya samo lauya.

Mai shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya daga sauraron karar sai zuwa ranar 4 ga watan Oktoban 2022.

Rahoto daga Labarun Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button