YAYA MACE ZATA KARE KANTA DAGA KAMUWA DA INFECTION NA MATA
YAYA MACE ZATA KARE KANTA DAGA KAMUWA DA INFECTION NA MATA

YAYA MACE ZATA KARE KANTA DAGA KAMUWA DA INFECTION NA MATA
Hanyoyin Da Zaki Bi Domin Kare Kanki:
1- Avoid Vaginal Douching : A cikin Farji akoi wassu kwayoyin bakteriya wadanda basa cutarwa kuma sunada amfani , amfaninsu shine suna taimakawa wajen bada kariya ga Farji , sai kaga wassu matan sukan wanke Farji da Sabulu ko detol haka , wadannan abubuwanda ake amfani wajen wanke farji yakan kashe bakteriya masu amfani na Farji , Sai masu cutarwa su samu daman shiga. A kiyaye wanke Farji Da Sabulu dakuma wadansu abubuwa Wanda bamusan Kansu ba.
2- Uses of Underwear : Amfani da wandon pants , wassu matan sukan bar wandonsu yayi datti , Barin datti ko amfani pant masu datti yakan bawa kwayoyin cuta daman shiga Farji.
A Tsaftace wanduna.
3- Cleaning Faeces : wajen wanke bahaya mafi yawa mata sukan dauki kwayar cutar da take dubura zuwa Farji, wanda basa yiwa dubura illa amma sukan yiwa Farji illah.
Shawara shine afara wanke Farji kafin a wanke dubura.
4- Sharing of Underwear: amfani da pants na wassu , ta yiu wacce kuke amfani da pants daya tanada cutar Sanyi idan kinyi amfani da nata kema zaki iya dauka.
Sai a kiyaye.
5- Sexual intercourse : mutun yakan iya daukan wannan cutar lokocin saduwa da namiji shawara itace adinga amfanida Condom lokocin saduwa..
Masu sauraranmu a Koda yaushe bayan Kun karanta wannan maganin zamu so karben a sahen mu na tsokaci.
Wani karamin yaro dan shekaru 7 ya rasa rayuwar sa sabida firgici bayan sojojin isra’ila sun biyo shi har gida
Palasdinawa mazauna yankin West Bank sun yi jana’izar wani karamin yaro mai shekaru bakwai a duniya mai suna “Rayan Suleiman”, kamar yadda “Labarun Hausa” ta ruwaito.
Mahaifan yaron sun bayyana cewa, tsoron sojojin Isra’ila ne yayi sanadiyyar rasuwar sa, a jiya ne dai sojojin Isra’ila suka biyo Rayan Suleiman da shi da ‘yan uwansa suna tafiya daga gida zuwa makaranta.
Sun yi ikirarin cewa, sojojin sun buga musu kofa cikin fushi sannan sukayi musu barazanar kamu, Rayan wanda dan karamin cikin yaran uku ya rasu lokaci kadan bayan aukuwar lamarin.
Mohammed Suleiman, wani dan uwan Rayan ya shaidawa AlJazeera cewa, bayan Rayan ya dawo gida, sojojin sun biyo shi inda suke ta masa magana cikin fushi.
Sojojin sun yi masa magana cikin fushi
cewa, shi mai jefa dutse ne yayi kacibus da wani soja bayan ya ruga, lokacin da Rayan yaga sojan a gaban sa ya firgita kawai sai ya fadi kasa cikin tsoro.
Mahaifin Rayan mai suna “Yasser Sulaiman” ya bayyana cewa, Rayan ya fadi kasa ne bayan yaga sojojin Isra’ilan da suka biyo shi sun bayyana a gaban kofar sa.
Yayyen Rayan ‘yan shekara takwas da
shekara goma sojojin sun yi musu
barazanar kamu, Hatsaniyar da ake yi ce ta sanya Rayan ya sume.
Duk da kokarin da likitoci suka yi a asibitin Beit Jala, ba a samu an ceto rayuwar sa ba.
Rahoto daga Labarun Hausa